in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta tabbatar da samar da karin guraben ayyukan yi a bana
2019-01-14 10:31:24 cri
Ma'aikatar harkokin jama'a da kula da zamantakewar al'umma ta kasar Sin ko MHRSS a takaice, ta ce gwamnati za ta dauki karin matakai na 他tabbatar da samar da guraben ayyukan yi ga Sinawa a wannan shekara ta 2019.

Wasu jami'an MHRSS sun shaidawa taron manema labarai cewa, gwamnati za ta ragewa kamfanoni nauyin lura da ma'aikata, yayin da a yanzu haka ake ci gaba da gudanar da bincike game da tsarin ragewa kamfanoni nauyin inshorar ma'aikatan da suke dauka aiki a fadin kasar.

Jami'an sun ce kamfanonin da ba su sallami ma'aikata daga bakin aikin su ba, za su iya karbar rabin kudin da suka biya a baya na inshorar rashin guraben ayyuka, domin karfafa masu gwiwa.

Wani jami'in gwamnatin kasar ta Sin ya bayyana cewa, a bana kasar za ta fuskanci karin matsin lamba na neman guraben ayyukan yi, duba da cewa sama da mutane miliyan 15 za su karu a kasuwar neman ayyuka ta biranen kasar, ciki hadda daliban da ake sa ran za su kammala jami'o'i kimanin su miliyan 8.34.

Wani taron koli na raya tattalin arzikin kasar Sin da ya gudana a watan Disambar bara, ya amince da kasancewar batun daidaita samar da guraben ayyukan yi, a matsayin batun dake sahun gaba, a jerin manufofin gwamnatin kasar Sin a shekarar ta 2019. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China