in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta mara bayan MDD don samar da kudaden tallafawa dakarun tsaron G5 na yankin Sahel
2019-01-11 10:14:23 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, a jiya Alhamis yace kasar Sin tana goyon bayan kudurin MDD don samar da tallafin kudade ga rundunar wanzar da tsaro ta hadin gwiwa ta G5 a yankin Sahel.

A yayin taron kwamitin sulhun MDD, Wu Haitao, mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD, ya bukaci kasa da kasa dasu kara taimakawa kasashen yammacin Afrika da yankin Sahel, a kokarin da suke na yaki da muggan laifuka da ta'addanci a kan iyakokin kasashen.

"Baki daya halin da ake ciki a yammacin Afrika da yankin Sahel akwai zaman lafiya, amma har yanzu kasashen suna fuskantar barazanar masu tsattsauran ra'ayin addini, da hare haren kungiyoyin 'yan ta'adda, da karuwar munanan laifuka da kuma bala'o'i daga idallahi", in ji shi.

Domin shawo kan wadannan kalubaloli, Wu ya ce magance wadannan matsaloli tun daga tushe shi ne abu mafi muhimmanci, don haka kamata yayi al'ummar kasa da kasa su mayar da hankali wajen taimakawa cigaban wadannan kasashen kana a taimaka musu wajen warware manyan kalubalolin da suka fi damunsu.

Da yake karkare jawabinsa, wakilin na kasar yayi alkawarin cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki da kasa da kasa wajen taka muhimmiyar rawa don samun nasarar wanzar da tsaro da zaman lafiya a nahiyar Afrika.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China