in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD:Tashin hankali na kassara ayyukan ma'aikatan jin kai a yankin arewa maso gabashin Najeriya
2019-01-11 09:34:27 cri
Ofishin MDD mai kula da harkokin jin kai ko OCHA a takaice, ya bayyana cewa, tashin hankali a yankin arewa maso gabashin Najeriya na kawo cikas ga ayyukan ma'aikatan jin kai, inda dubban daruruwan mutanen da rikici ya raba da muhallansu ke bukatar taimako.

Mai magana da yawun babban sakataren MDD Stephane Dujarric ya bayyana cewa, ma'aikatan OCHA sun bayyana cewa, tun a watan Nuwamban shekarar da ta gabata, an janye ma'aikatan jin kai 260 daga yankunan dake fama da tashin hankali, lamarin da ya katse taimakon jin kai da ake baiwa dubban daruruwan mutanen dake bukatarsa.

Da yake yiwa taron manema labarai karin haske kan lamarin, Dujarric ya ce, yayin da wasu ma'aikatan jin kan suka fara komawa wuraren aikinsu, rashin tsaro kuma na kawo cikas ga gudanar ayyukan jin kai kamar yadda aka saba.

Mai magana da yawun hukumar OCHA a Najeriya Erdward Kallon ya bayyana damuwa kan yadda tashin hankali a yankin arewa maso gabashin kasar ya raba mutane da dama da matsugunansu.

OCHA ta ce, ma'aikatan agaji 260 da aka janye, ita ce mafi yawa da hukumar ta yi, tun lokacin da ta fara kawo dauki a shekarar 2016.

Hukumar ta ce, sama da mutane miliyan 7 ne ke matukar bukatar taimako, sakamakon yakin da aka kwashe shekaru 10 ana tafkawa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China