Shugaba Xi ya ce, ya yi bakin ciki da jin labarin aukuwar wannan bala'in nan na tsunami, wanda ya yi sanadiyyar hasarorin rayuka da kadarori, kuma a madadin gwamnatin kasar Sin da al'ummarta da kuma shi kansa, yana mika ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasu da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.
Shugaban ya kuma yi fatan al'ummar kasar Indonesia za su gaggauta farfado da kasarsu, a karkashin gwamnatin kasar mai ci.(Lubabatu)