in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wu Haitao ya yi kira ga kasa da kasa da su tallafawa wasu yankunan Afirka a fannin yaki da manyan laifuka
2018-12-20 10:48:22 cri
Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa, da su tallafawa yankunan yammaci da tsakiyar Afirka da horon kwarewa, da sanin makamar aiki, a kokarin su na shawo kan kalubalen manyan laifuka tsakanin kasashen yankunan.

Wu Haitao, ya yi wannan kira ne yayin zaman kwamitin tsaron majalissar na jiya Laraba. Ya ce ci gaba da fuskantar wannan matsala ga kasashen, na barazana ga ci gaban su, da zamantakewar al'ummun su, tare da rura wutar tashe tashen hankula, da yaduwar ayyukan ta'adanci.

Ya ce batun fataucin miyagun kwayoyi, na bukatar hadin gwiwar kasashen duniya, da sauke nauyi daga ko wane bangare. Kaza lika akwai bukatar rufe kasuwannin kwayoyi, da hana shan su, da samar da su, da hada hadar su tun daga tushe.

Wu Haitao ya kara da cewa, ya zama wajibi a karfafa tsare tsaren aiwatar da manufofi tsakanin yankuna, da hukumomin kasa da kasa, da ma na MDD, ta yadda za a rika aiki tare. Ya ce Sin ta nuna yabo ga kokarin da suke yi wajen yaki da hada hadar miyagun kwayoyi, da tabbatar da aiwatar da dokoki masu nasaba da hakan, karkashin ka'idojin kasa da kasa. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China