in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in Diflomasiyya: Dakatar da takaddamar sanyawa juna haraji da Sin da Amurka suka yi ya dace da muradun kasashen biyu
2018-12-12 15:33:23 cri
Karamin jakadan ofishin jakadancin kasar Sin dake San Francisco na kasar Amurka Wang Donghua, ya bayyana cewa, yadda kasashen Sin da Amurka suka dakatar da takaddamar sanyawa juna haraji, ya rage zaman dar-dar da ake yi kan ci gaban tattalin arziki da dorewar kasuwanni a kasashen biyu da ma ragowar sassan duniya.

Jami'in wanda ya bayyana hakan cikin wani sharhin da ya rubuta mai taken "An yi maraba da dakatar da takaddamar Sin da Amurka na sanyawa juna haraji" wanda aka wallafa jiya Talata a jaridar nan ta San Francisco Chronicle, ya ce, matakin da kasashen biyu suka dauka labari ne mai dadin ji ga tattalin arziki game da kasuwannin duniya. Shugabannin kasashen Sin da Amurka dai sun gana tare da cin abincin dare a gefen taron kolin kungiyar G20 da ya gudana a kasar Argentina.

A yayin da zaman cin abincin daren, shugaba Xi Jinping na kasar Sin da takwaransa na kasar Amurka Donald Trump sun amince ba za su kara sanyawa juna wani sabon haraji ba. Ya kamata a ce kasashen biyu za su magance bambance-bamnbancen dake tsakaninsu, duba da yadda sassan biyu ke amfana da juna a fannin tattalin arziki.

Jami'in na kasar Sin ya kara da cewa, galibin Amurkawa da ya tattauna da su, suna fatan za a hanzarta kawo karshen takaddamar cinikayyar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma magance kara kawo wa kamfanonin Amurka illa sakamakon harajin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China