in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani babban jami'in gwamnatin kasar Sin ya yi kira ga kasashen duniya su kara goyon-bayan dabarun ci gaba na kasar Sin
2018-12-10 10:19:27 cri
Wani babban jami'in jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya yi kira ga kasashen duniya da su kara bayar da hikima da goyon-baya ga kasar Sin wajen aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje.

Huang Kunming, wanda shi ne memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban sashin fadakar da jama'a na kwamitin tsakiya na jam'iyyar, ya yi wannan furuci ne yayin da yake ganawa da wasu kwararru da masana daga kasashen waje a gun taron karawa juna sani dangane da darrusan tattalin arziki dake tattare da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje da kasar Sin ta fara aiwatarwa shekaru 40 da suka gabata, wanda aka yi jiya Lahadi, a jami'ar Tsinghua dake birnin Beijing.

Huang ya bayyana cewa, manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje ba taimakawa ci gaban kasar Sin kadai ta yi ba, har ma da samar da alfanu ga duk duniya baki daya. Ya ce Sin za ta ci gaba da tsayawa kan aiwatar da wannan muhimmiyar manufa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China