in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Somaliya ta sanya hannu kan shirin MDD na yaki da cin hanci
2018-12-10 09:43:50 cri
Kasar Somaliya ta bi sahun sauran kasashen duniya wajen shirya bikin ranar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa da kasa tare da sanya hannu kan shirin MDD na yaki da wannan matsala a kasar.

Ma'aikatar shari'ar kasar da shirin raya kasashe na MDD (UNDP) ne suka sanya hannu kan shirin na PIP, da nufin kara karfin hukumomin gwamnati na yaki da cin hanci da karfafa kula da dukiyar al'umma.

A jawabinsa yayin bikin kaddamar da shirin da MDD ke marawa baya, ministan shari'a na kasar Somaliya Hassan Hussein Haji ya bayyana cewa, kasarsa na shirin kara hukumar yaki da cin hanci, don haka suna bukatar sakatariya, da horaswa da ma taimako a dukkan fannoni.

Ya kuma bayyana jerin matakan da gwamnati ke dauka na jaddada kudurinta na yaki da cin hanci da rashawa da gudanar da ayyuka a bayyane domin gina hukumomin da za su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Ya ce, musamman ma aikin zai karfafa gudanar da ayyuka bisa doka a wasu muhimman hukumomin kasar, kamar ofishin babban mai binciken kudi na kasar da sauransu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China