in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta gabatar da korafi kan yadda aka tsare babbar jami'ar kamfanin Huawei
2018-12-10 09:37:35 cri
A jiya ne mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Le Yucheng ya gayyaci jakadan Amurka dake nan kasar Sin Terry Branstad, ya kuma gabatar da korafi da ma yin Allah wadai da kakkausar murya kan yadda Amurka ta umarci hukumomin Canada su tsare babbar jami'ar kamfanin fasahar sadarwa na Huawei babu gaira ba dalili.

Da yake karin haske cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, Mr. Le ya bayyana cewa, abin da Amurkar ta yi, ya saba wa 'yanci da muradun al'ummar kasar Sin kana ba ya bisa turba.

Jami'in ya ce, kasar Sin ta yi Allah wadai da matakin na Amurka,don haka tana kira ga bangaren Amurka da ya dora muhimmanci kan matsayin kasar Sin ya kuma gaggauta daukar matakan da suka dace don gyara kura-kuran da ya tafka, ya kuma janye sammacin kama 'yar kasar Sin da ya bayar.

Le ya ce, kasar Sin za ta mayar da martani kan matakin da bangaren Amurkar zai dauka.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China