in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta karrama mutane 100 bisa gudummawar su a fanni aiwatar da gyare gyare cikin gida da bude kofa ga ketare
2018-11-26 21:13:41 cri
Mahukuntan kasar Sin sun tabbatar da shirye shiryen da ake yi, na karrama wasu Sinawa 100, saboda gudummawar su a fanni aiwatar da gyare gyare a cikin kasar, tare da bude kofa ga ketare.

An dai zabo mutanen ne daga sassan rayuwa daban daban, sun kuma samu shaida daga matakai na tushen al'umma, kana an gudanar da tantancewa domin tabbatar da sahihancin zaben na su.

Wadanda za a karrama din sun kunshi masana a fannin kimiyya, da masana tattalin arziki, da 'yan JKS da suka yi fice a matakai na tushe, da wadanda suka yi fice a fannin kwadago. Sauran sun kunshi manajojin kamfanoni, da mamallaka sana'o'i masu zaman kan su.

A bana ne dai kasar Sin ke cika shekaru 40, tun bayan fara aiwatar da manufofin gyare gyare a cikin kasar, da kuma bude kofar ta ga sauran kasashen duniya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China