in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 25 ne suka rasu sakamakon fashewar wasu abubuwa a tsakiyar Somalia
2018-11-26 21:10:28 cri
A kalla mutane 25 aka tabbatar da rasuwar su, baya ga wasu da dama da suka jikkata da sanyin safiyar Litinin din nan, sakamakon wasu tagwayen fashewa da suka auku a yankin Galkayo dake tsakiyar kasar Somalia.

Rahotanni daga yankin sun ce, mayakan Al Shabab ne suka kaddamar da hari kan wata cibiya, ta wani malamin addinin musulunci mai suna Sheikh Abdiweli Ali Elmi, bayan da mayakan kungiyar suka zarge shi da furta wasu kalamai na tozarta Annabi Mohammad.

Tuni kuma Al-Shabab ta ayyana daukar alhakin kaddamar da wannan hari.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China