in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta shirya taron inganta ayyukan kakakin hukumomi
2018-11-26 10:13:35 cri
A jiya Lahadi ne, aka kaddamar da wani taron tattaunawa kan yadda kakakin hukumomi za su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Ofishin yada labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin, da kwalejin nazarin ilmin yada labaru na jami'ar Peking ne suka shirya wannan taro cikin hadin gwiwa, inda masu magana da yawun hukumomin kwamitin kolin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da na gwamnatin tsakiya da na gwamnatocin larduna da wasu manyan masana'antu mallakar gwamnatin kasar Sin da wasu masana da kuma jagororin kafofin yada labaru suka halarci wannan taro.

A yayin taron, Mr. Xu Lin, mataimakin shugaban hukumar yayata ayyukan kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya bayyana cewa, aikin yada labaru ya samu ci gaba ne a nan kasar Sin a kai a kai a yayin da ake aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare. A cikin shekaru 40 da suka gabata, aikin yada labaru ya inganta a fili bisa ka'idar girmama dan Adam sakamakon hakan, aikin ya zama wata muhimmiyar hanyar kara yin mu'amala tsakanin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin kasar da jama'a fararen hula. Sannan ana yada labaru ne bisa ka'idar kara yin mu'amala da ketare domin tabbatar da ganin sauran kasashen duniya sun fahimci kasar Sin. Bugu da kari, masu aikin yada labaru su ma sun samu ci gaba, inda suka zama wata kafa dake watsa wa sauran kasashen duniya kyawawan labaru game da kasar Sin.

A farkon shekarun 80 ne, gwamnatin kasar Sin ta kafa tsarin yada labarunta ga waje a hukumance. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China