in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tattaunawa da Tijjani Inuwa Babura jami'in ma'aikatar masana'antu da cinikayya da zuba jari ta Najeriya
2018-11-15 15:04:10 cri


A kwanakin baya ne, aka yi wani gagarumin bikin baje-koli a birnin Shanghai dake gabashin kasar Sin, wato bikin baje-kolin kayayyakin kasa da kasa da ake shigowa da su kasar Sin karo na farko, ko kuma CIIE a takaice, wanda ya samu halartar kamfanoni sama da 3600 daga kasashe da yankuna sama da 170 a duk fadin duniya, ciki har da wasu daga kasashen Afirka.

A yayin da ake gudanar da wannan biki, wato ranar 8 ga watan Nuwamba, tawagar ma'aikatar masana'antu da cinikayya da zuba jari ta Najeriya da ta zo birnin Shanghai ta hada kai da karamin ofishin jakadancin Najeriya dake Shanghai, don shirya wani dandalin tattaunawa kan harkokin cinikayya da zuba jari, wato Nigeria Trade and Investment Forum 2018. Dandalin ya samu halartar jami'ai daga ma'aikatar masana'antu da cinikayya da zuba jari ta Najeriya, da jami'an diflomasiyyar Najeriya dake Beijing da Shanghai da Guangzhou da Hong Kong, da 'yan kasuwa da kamfanonin Najeriya dake kasar Sin, tare kuma da takwarorinsu na kasar Sin wadanda ke da niyyar zuba jari a Najeriya.

A nasa bangaren, babban sakataren ma'aikatar masana'antu da cinikayya da zuba jari ta Najeriya, Mista Sunday Edet Akpan ya bayyana cewa, Najeriya na da kyakkyawan yanayin zuba jari da gudanar da kasuwanci, inda ya yi maraba da 'yan kasuwa da kamfanonin kasar Sin da su je Najeriyar don su zuba jari.

A wajen dandalin tattaunawar, wakilinmu Murtala Zhang ya samu damar zantawa da daya daga cikin membobin tawagar ma'aikatar masana'antu da cinikayya da zuba jari ta Najeriya wadanda suka zo birnin Shanghai, wato Malam Tijjani Inuwa Babura, darekta mai kula da manufofi da tsare-tsare da bincike gami da yin kididdiga a ma'aikatar, inda ya bayyana makasudin ziyararsu Shanghai, da yadda ma'aikatarsu take kokarin bunkasa harkokin cinikayya da zuba jari tsakanin Sin da Najeriya.

Ga yadda tattaunawar tasu ta kasance.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China