in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masani: CIIE wata babbar dama ce ga hajojin Afirka ta shiga kasuwannin duniya
2018-11-07 20:15:13 cri
Darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin dake Abuja,babban birnin Najeriya Charles Onunaiju ya bayyana cewa, bikin baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin CIIE dake gudana yanzu haka a birnin Shanghai, wata muhimmiyar kafa ce da za ta baiwa nahiyar Afirka damar tallata hajojinsu a kasuwannin duniya.

Da yake karin haske yayin wata zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, Charles Onunaiju ya bayyana cewa, bikin na CIIE ya samar da wata babbar kasuwa mai bukatar hajoji, inda ya bayyana bikin na CIIE wanda shi ne irinsa na farko a matsayin, kasuwar duniya.

A cewarsa, idan kasashen dake wakiltar nahiyar Afirka suka yi kyakkyawan tasiri a yayin bikin baje kolin, hakan zai ba da babbar dama ga karin kasashen Afirka.

A yayin bikin baje kolin, Najeriya, kasa mafi karfin tattalin arziki a Afirka, tana baje kolin albarkatun ma'adinai da mai da iskar gas da fina-finai da wakoki da ma kayayyakin amfanin gona da Allah ya hore mata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China