#CIIE# Kasar Sin za ta shigo da kayayyaki da ayyukan hidima masu darajar dala biliyan 40000 a shekaru 15 masu zuwa
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a yau Litinin a birnin Shanghai cewa, an kimanta cewa, a shekaru 15 masu zuwa, kasarsa za ta shigo da kayayyaki, da ayyukan hidima masu darajar dalar Amurka biliyan 30000 da biliyan 10000, kaza lika Sin za ta inganta bude kofa ga kasashen ketare ta fuskoki guda biyar, ciki har da inganta karfin shigo da kaya, da sassauta izinin zuba jari a Sin, da kafa muhallin cinikayya mai kyau kwarai a duniya, da habaka sabbin fannonin da za a bude kofa a kai, da kuma inganta hadin kai na bangarori da dama, da tsakanin bangarori biyu da dai sauransu. (Bilkisu)