in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani rahoton ya bayyana cewa Afrika ta jawo karin jarin kasashen waje
2018-10-30 10:54:38 cri
Wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya samu, ya bayyana cewa nahiyar ta samu karuwar jarin kai tsaye daga kasashen waje (FDI) a shekarar 2017, inda Afrika ta kudu da Morocco suka zama wurare da suka fi samun jari.

Rahoton jan jari na Afrika da Ernst & Young, da kamfanin tuntuba kan harkokin hada-hadar kudi ya hada, ya ce a bara, nahiyar Afrika ta samu ayyukan zuba jari 718, wanda ya karu da kaso 6 kan na bara waccan, bisa farfadowar tattalin arzikin nahiyar.

Rahoton, ya kuma bayyana kasashen da suka fi samun jarin, inda Habasha da Kenya da Zimbabwe suka samu gagrumin ci gaba a wannan fanni.

Afrika ta kudu da Morocco ne suka kasasnce matsayi guda na jagoran kasashen da suka fi samun jarin.

Rahoton ya kuma gano cewa, Afrika ta Kudu da Morocco da Kenya da Nijeriya da Habasha, su ne wadanda suka fi karfin tattalin arziki a yankunan da suke, wanda tattalin arzikinsu baki daya, ya mamaye kaso 40 na nahiyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China