Sakamakon zaben na ta, Zewde ta zamo mace ta farko da za ta shugabanci kasar dake gabashin Afirka. Tuni dai shugaba Zewde ta sha rantsuwar kama aiki a yau, gaban mambobin majalissun dokokin kasar biyu.
Cikin jawabin ta, ta yi alkawarin yin iyakacin kokarin, ta wajen bautawa kasar ta da al'ummar ta.