in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya jaddada bukatar gina yankunan ciniki maras shinge
2018-10-24 21:03:07 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada bukatar ci gaba da gina yankunan cinikayya maras shinge, a wani mataki na kara fadada kudurin kasar, na aiwatar da kwaskwarima a gida, da bude kofa ga kasashen ketare a sabon zamanin da ake ciki.

Shugaba Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, ya yi wannan tsokaci ne, yayin da yake gabatar da umarni, game da bunkasa ginin yankunan ciniki maras shinge na kasar ta Sin.

Ya ce bunkasar wadannan yankunan ciniki, daya ne daga muhimman matakan da kwamitin koli na JKS ke dauka, wajen fadada gyaran fuska, da kara bude kofa ka kasashen waje a sabon zamani da ake ciki, ya kuma zama wani jigo na cimma nasarar hakan.

Shugaban ya kara da cewa, bayan shekaru 5 da aiki tukuru, a fannin bunkasa yankunan cinikayya cikin 'yanci na Sin, an kai ga cimma manyan nasarori, wadanda suka baiwa kasar damar tunkarar matakan inganta harkokin gudanarwa.

Daga nan sai shugaban na Sin ya ja hankalin masu ruwa da tsaki a fannin, da su dauki karin matakan hanzarta ci gaban yankunan cinikayya cikin 'yanci, ta yadda hakan zai inganta kirkire kirkire, wadanda za su kai ga cimma manyan burikan kasar guda biyu na shekaru 100, da kuma na sake farfado da kasar baki daya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China