Rahotanni na cewa an dauki matakin rufe jami'ar ne, bayan barkewar tashin hankali a jiya Litinin, da nufin dakile kara tabarbarewar yanayin tsaro. Tun da fari dai daliban jami'ar sun yi boren ne, domin nuna kin jinin abun da suka kira murzunawa dalibai da mahukuntan jami'ar ke yi. Sai dai kuma daga bisani bore ya rikide zuwa tashin hankali, wanda ya haifar da lalata wasu babura da motoci, da gine ginen jami'ar.