in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane a kalla 19 suka mutu sakamakon fashewar bom a kwalejin fasaha da sana'a ta Kerch
2018-10-18 13:23:54 cri
An samu fashewar bom da harbe-harbe a kwalejin fasaha da sana'a ta Kerch dake gabashin zirin Crimea, wadanda suka haddasa rasuwar mutane a kalla 19 yayin da wasu 47 suka ji rauni.

Gwamnan yankin Crimea ya bayar da sanarwa a kafofin watsa labaru na sada zumunta a wannan rana cewa, wanda ya kitsa lamarin wani dalibi ne dan aji hudu a kwalejin wanda tuni ya riga ya kashe kansa, an gano gawarsa a dakin karatu na kwalejin. Har yanzu dai ana ci gaba da bincike kan lamarin.

A wannan rana kuma, shugaban kasar Ukraine Petro Poroschenko ya gabatar da jawabi, inda ya zargi lamarin fashewar bom din da harbe-harben, a cewarsa wannan ne kisan gilla mai ban tsoro.

Kafin haka, kwamitin bincike na tarayyar Rasha ya yi aikin bincike kan lamarin bisa dokokin shari'a na kai farmakin ta'addanci, daga baya kuma ya sake gudanar da aikin bincike kan lamarin bisa dokokin shari'a na kisan gilla.

A watan Maris na shekarar 2014, an jefa kuri'ar raba gardama a yankunan Crimea da Sevastopol, masu jefa kuri'a sama da kashi 90 cikin 100 sun amince da ballewa daga Ukraine da komawa kasar Rasha. Amma, kasar Ukraine ba ta amince da hakan ba, tana adawa da ficewar yankunan biyu zuwa kasar Rasha. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China