Yayin da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da babban taro karo na tara tsakanin kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar yaki da miyagun laifuffukan da aka aikata tsakanin kasashe daban-daban ta MDD, Wang Qun ya ce, kamata ya yi kasashe daban-daban su sauke nauyin dake wuyansu bisa yarjejeniyar, da girmama dokoki gami da hakkin kowace kasa na yaki da miyagun laifuffukan da aka aikata, tare kuma da tabbatar da aiwatar da wannan yarjejeniya cikin adalci kuma ta hanyar da ta dace.
Wang ya kara da cewa, kasar Sin na goyon-bayan kwararru masu yaki da miyagun laifuffukan da aka aikata ta kafar Intanet da su ci gaba da gudanar da ayyukan hadin-gwiwa a wannan fanni.(Murtala Zhang)