in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar UN-Habitat: Ya kamata a koyi fasahar kasar Sin wajen kula da muhallin zaman al'umma
2018-10-02 15:40:58 cri

Jiya Litinin, rana ce da MDD ta kebe domin lura da batun muhallin zaman al'umma. Albarkacin wannan rana ta musamman, shirin MDD mai kula da muhallin zaman al'umma (UN-Habitat), ya shirya wani biki, na ba da kyautar karramawa a hedkwatarsa dake Nairobin kasar Kenya.

A wajen bikin, birnin Xuzhou na kasar Sin, ya samu kyautar yabo, bisa ci gaban da ya samu a fannin sauya tsare-tsaren birnin, tare da neman ci gaban tattalin arzikinsa.

Da take tsokaci a yayin bikin, shugabar shirin UN-Habitat Maimunah Mohd Sharif, ta ce ya kamata a yada fasahohin ci gaba, da kasar Sin da sauran wasu kasashe suka samu, a fannin kula da muhallin zaman al'umma, musamman ma ga kasashen dake kan hanyar tasowa, wadanda suke fuskantar dimbin kalubaloli a wannan fanni. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China