in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin jakadancin Sin dake Najeriya ya shirya liyafar murnar cika shekaru 69 da kafa Jamhuriyar Jama'ar kasar Sin
2018-09-28 19:34:14 cri

Jiya Alhamis, mukaddashin jakadan kasar Sin dake Najeriya, Lin Jing, ya shirya wata liyafa a Abuja, fadar mulkin Najeriya, domin murnar cika shekar 69 da kafa Jamhuriyar Jama'ar kasar Sin. Wasu jami'an gwamnatin tarayyar Najeriya, da jakadun kasashen waje dake kasar, da wakilan kamfanonin kasar Sin dake kasar sama da dari uku sun halarci liyafar.

A jawabinsa, Lin Jing ya ce, a shekarar da muke ciki, an yi nasarar gudanar da taron kolin dandalin tattaunawar hadin-gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC a birnin Beijing, inda shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya halarci taron, har ma ya gana da shugaban kasar Sin Xi Jinping. Hadin-gwiwar dake tsakanin Sin da Najeriya ta kasance abun misali ga hadin-gwiwar Sin da sauran wasu kasashen Afirka.

Shi kuma a nasa bangaren, mataimakin babban sakataren ma'aikatar harkokin wajen Najeriya, Lawan Gana wanda ya halarci liyafar, ya bayyana cewa, bana shekaru 47 ke nan da kulla dangantakar diflomasiya tsakanin Sin da Najeriya, Najeriya na maraba da kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasar, kana tana fatan karfafa hadin-gwiwa da gwamnatin kasar Sin a fannoni daban-daban.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China