Kimanin mayakan kungiyar al-Shabaab 35 aka hallaka da kuma jikkata wasu da dama bayan musayar wuta tsakaninsu da dakarun sojojin gwamnatin Somaliya wadanda ke samun taimakon dakarun tsaron kungiyar tarayyar Afrika AU a garin Qoryoley, a shiyyar Lower Shabelle, dake kudancin Somalia, in ji jami'in kasar Somaliya.
Guda daga cikin sojojin Somaliya ya rasa ransa kana wasu sojojin biyu kuma sun samu raunuka a lokacin da aka yi mummunar arangama da mayakan na al-Shabaab a cikin dare, mataimakin gwamnan lardin Qoryoley, Abdi Ahmed Ali ne ya bayyana hakan ga manema labarai. (Ahmad Fagam)