in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya da AfDB za su taimakawa Ghana wajen kawar da wuraren bahaya a bainar jama'a
2018-09-20 10:41:34 cri
Mataimakin ministan tsaftar muhalli da albarkatun ruwa na kasar Ghana Patrick Boamah ya sanar da cewa, gwamnatin kasar ta ware dala miliyan 93 don taimakawa wajen magance al'adar nan ta bahaya a bainar jama'a a birane da yankunan karkarar kasar.

Daga cikin wannan adadi, za a yi amfani da dala miliyan 48 da bankin duniya zai bayar wajen raya ayyukan inganta rayuwar jama'a, wadanda suka hada da samar da magewayi a gidajen jama'a da ma'aikatu a babban birnin kasar da a kalla mutane miliyan 3.7 za su iya amfani da su.

Za kuma a yi amfani da dala miliyan 45 da bankin raya Afirka(AfDB) zai bayar wajen gudanar da aikin tsaftar muhalli a yankunan karkara daga shekarar 2017 zuwa 2019, ciki har da gina wuraren bahaya 20,000 a gidajen iyalai a al'ummomi 500 a yankuna shida na kasar.

Hukumar lafiya ta duniya(WHO) da asusun tallafawa kananan yara na MDD(Unicef) da shirin nan na sanya ido(JMP) sun sanya kasar ta Ghana a matsayin kasa ta 7 da ba ta da magewayi mai kyau a duniya, inda kimanin kaso 14 cikin 100 na 'yan kasar ne kadai ke iya amfani da magewayi .(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China