in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin na fatan karfafa hadin-gwiwar bangarori daban-daban don shimfida zaman lafiya a zirin Koriya
2018-09-18 16:52:01 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin dake Majalisar Dinkin Duniya, jakada Ma Zhaoxu ya bayyana jiya Litinin cewa, yana fatan bangarori masu ruwa da tsaki za su karfafa hadin-gwiwa tsakaninsu, da sassauta matsalar dake addabar zirin Koriya, da tabbatar da shimfida dauwamammen zaman lafiya da kwanciyar hankali a wurin.

A wajen wani taro kan batun nukiliya na zirin Koriya da kwamitin sulhun MDD ya shirya, jakada Ma ya ce, Sin na goyon-bayan Amurka da Koriya ta Arewa su daidaita matsalar makamashin nukiliya na zirin Koriya ta hanyar yin shawarwari, haka kuma Sin na fatan kasashen biyu za su tabbatar da nasarorin da aka samu a wajen shawarwarinsu. Ma ya ce, kasar Sin na goyon-bayan kara yin mu'amala da shawarwari tsakanin Koriya ta Arewa da ta Kudu, tana kuma fatan shugabannin kasashen biyu za su yi shawarwari cikin nasara a Pyongyang.

Har wa yau, Ma ya ce, kasar Sin ta yaba matuka ga kokarin da Koriya ta Arewa ta yi wajen kawar da makaman nukiliyarta gami da tabbatar da samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin Koriyar. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China