in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Abbas: Kashe kashe, kwace muhallai da lalata matsugunai ba zai haifar da zaman lafiya ba
2018-09-17 10:48:52 cri
Shugaban Palestinawa Mahmoud Abbas ya fada a jiya Lahadi cewa, kashe kashe da kara gina matsugunai da kuma lalata matsugunan al'ummar Palastinawa ba zai samar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya ba.

Abbas yayi wannan tsokaci ne a lokacin ganawa da wata tawagar da ke wakiltar tsoffin mambobi masu tsattsauran ra'ayi na majalisar kasar Israeli, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na WAFA ya ambata.

Abbas ya duba irin cigaban siyasa na baya bayan nan da aka samu, da kuma irin mummunan halin da ake ciki a sanadiyyar matakan da Israila ke dauka da kuma irin goyon bayan da take samu daga gwamnatin Amurka, inji WAFA.

Tun da farko a wannan rana, wakilin musamman na MDD kan batun zaman lafiyar yankin gabas ta tsakiya Nickolay Mladenov, ya gargadi Israel dangane da rusa kauyen Al Khan Al-Ahmar Bedouin dake gabashin birnin kudus.

A wata sanarwa da aka aike wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua, Mladenov, ya bukaci hukumomin Isra'ila da kada su cigaba da rusa matsugunan al'ummar Palastinawa a yammacin kogin Jordan.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China