in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da zaben majalisun kananan hukumomin Libya
2018-09-17 10:05:34 cri
Ofishin MDD a Libya (UNSMIL) yayi maraba da zabukan majalisun kananan hukumomi a Libya, inda ya bayyana shi da cewa wani muhimmin mataki ne ga kasar Libya na tabbatar da tsarin mulkin dimukradiyya a kasar.

UNSMIL ya fada cikin wata sanarwa cewa, yayi maraba da zaben majalisun yankunan Bani Walid da Derj. Kwamitin shirya zabukan majalisun kananan hukumomin ya cancanci yabo saboda shirya zaben, inji sanarwar.

Shirin raya cigaba na MDD (UNDP) a Libya, ya sanar a ranar Asabar cewa, Jamus zata samar da euro miliyan 2 kwatankwacin dala miliyan 2.33 ga kasar Libya domin shirya zabuka tsakanin shekarun 2018 zuwa 2020, yayin da hukumar shirya zabukan majalisun yankunan (CCMCE) ta sanar da fara zabukan a biranen Bani Walid da Derj dake kudu maso yammacin Libya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China