in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar sufurin Sin ta yi kira da karfafa matakan kandagankin mahaukaciyar guguwar Mangkhut
2018-09-17 09:43:02 cri
Mataimakin ministan harkokin sufuri na kasar Sin He Jianzhong ya yi kira da a kara daukar matakan da suka dace don tunkarar mahaukaciyar guguwar nan mai tafe da ruwa da iska mai karfi ta Mangkhut wadda ta isa yankin gabar kudancin kasar jiya Lahadi da yamma.

Yayin wani taron manema labarai ta kafar bidiyo, ma'aikatar sufurin kasar ta kuma bukaci hukumomi sufurin kasa da na ruwa dake yankin da mahaukaciyar guguwar ta ratsa da su dauki matakan kariya.

Da misalin karfe 5 na yammcin jiya ne mahaukaciyar guguwar ta Mangkhut ta isa gabar birnin Jiangmen na lardin Guangdong dake kudancin kasar Sin, kafin daga bisani ta nausa zuwa arewa maso yamma sannan ta shiga jihar Guangxi mai cin gashin kanta ta kabilar Zhuang.

Rahotanni na cewa, kusan dukkan harkokin sufuri sun tsaya cik a gabar biranen dake lardin Guangdomg a jiya Lahadi, kana an rufe manyan hanyoyi dake gabar ruwa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China