in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin MDD sun shirya bikin murnar ranar hadin-gwiwar kasashe masu tasowa
2018-09-13 11:05:02 cri
An yi bikin murnar ranar hadin-gwiwar kasashe masu tasowa jiya Laraba, a ofishin kwamitin kula da harkokin tattalin arziki da zamantakewar al'umma na kasashen Asiya da Pasifik na Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin Bangkok na kasar Thailand, inda aka taya juna murnar hadin-gwiwar kasashe masu tasowa, saboda nasarori da dama da suka samu wajen neman samun dauwamammen ci gaba.

Kwamitin kula da harkokin tattalin arziki da zamantakewar al'umma na kasashen Asiya da Pasifik na Majalisar Dinkin Duniya, da ofishin kula da harkokin hadin-gwiwar kasashe masu tasowa na MDD, gami da ma'aikatar harkokin wajen kasar Thailand su ne suka shirya wannan biki cikin hadin-gwiwa, da nufin murnar cika shekaru arba'in da amincewa da shirin daukar matakai na Buenos Aires, a wajen babban taron hadin-gwiwar kasashe masu tasowa ta fannin fasahohi na MDD.

Da yake jawabi kan hakan, jakadan kasar Sin dake kasar Thailand, Lv Jian ya ce, kamata ya yi kasashe masu tasowa su ci gaba da zurfafa hadin-gwiwarsu, don samar da muhimmin karfi ga ci gaban duk duniya.

Ya ce Sin kasa ce dake taimakawa wajen inganta hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, wadda ta dade tana nuna goyon-baya, gami da halartar ayyukan hadin-gwiwa tare da sauran kasashe masu tasowa a fannoni daban-daban.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China