in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta bukaci asibitoci su rika duba wadanda aka harba da bindiga ba tare da neman shaidar izininta ba
2018-09-08 16:17:23 cri
Rundunar 'yan sandan Nijeriya, ta yi kira da asibitoci da kada su ki duba wadanda suka ji rauni sanadiyyar hatsari ko harbin bindiga saboda rashin izini daga gareta.

Edet Okon, Kakakin rundunar 'yan sanda jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar, ya ce babu bukatar neman izinin rundunar kafin duba wadanda suka yi hatsari ko suka ji rauni sanadiyyar harbin bindiga.

Sanarwar da kakakin ya fitar a jiya, ta ce rundunar na son gyara wannan kuskure da ake yi, dake hana bada kulawa ga wanda ya yi hatsari ko ya samu rauni daga harbin bindiga, idan babu shaidar izinin rundunar.

A cewarsa, bisa darajar da take ba ran bil adama, rundunar 'yan sandan ta na kira ga dukkan asibitoci da cibiyoyin lafiya, su rika karbar irin wadancan marasa lafiya don gaggauta ba su kulawa da nufin ceton rayuka.

Sai dai ya ce, yayin da ake ba su kulawa, dole ne a gaggauta kai rahoto ga 'yan sanda domin gudanar da bincike da daukar matakan da suka dace. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China