in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gabatar da sakon taya murnar bude dandali game da cikar shawarar ziri daya da hanya daya shekaru 5
2018-09-07 19:41:55 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da sakon taya murnar bude dadandalin tattaunawa na kasar Kazakhstan, game da cikar shawarar ziri daya da hanya daya shekaru 5.

Shugaba Xi Jinping ya gabatar da sakon ne a Juma'ar nan ta kafar bidiyo. Ya ce wannan shawara ta samu matukar karbuwa tsakanin kasashe masu tarin yawa.

Shugaban na Sin ya kara da cewa, kasashen da suka amince su shiga a dama da su a cikin shawarar, suna ci gaba da tuntubar juna a wajen tsara manufofi, da gaggauta aiwatar da shirye-shiryen da suka shafi raya tattalin arziki da cinikayya. Har ila yau suna mai da hankali matuka wajen hade sassan manyan ababen more rayuwa, da bunkasa hadin gwiwa a bangaren raya masana'antu da hada hadar kudade, da karfafa musaya tsakanin al'umma, matakan dake haifar da tarin alfanu ga jama'ar kasashen.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China