Da yammacin ranar 3 ga watan Satumba ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya gabatar da wani muhimmin jawabi a yayin bude taron kolin FOCAC na Beijing 2018 inda shugaban ya tabo batutuwa masu yawa da suka shafi hulda tsakanin Sin da kasashen Afrika da yadda za'a kyautata mu'amala da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu daga dukkan fannoni, jawabin na shugaba Xi Jinping ya ja hankalin shugabani da wakilan kasashen Afrika da suka halarci taron kolin, Hadi Sirika shi ne karamin ministan sufurin jiragen saman Najeriya a zantawarsa da wakilin sashen Hausa na gidan radiyon kasar Ahmad Inuwa Fagam ya yi tsokaci game da jawabin na shugaba Xi.