in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#FOCAC#An bude taron kolin Beijing na FOCAC
2018-09-03 17:10:48 cri

Yau Litinin da yamma, aka bude taron koli na dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka na shekarar 2018 wato FOCAC a birnin Beijing, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da muhimmin jawabi.

Shugabanni ko wakilai na kasashen Afirka 53, da babban sakataren MDD Antonio Guterres, shugaban hukumar zartarwar kungiyar tarayyar Afirka AU Moussa Faki Mahamat, da masu sa ido da suka fito daga kungiyoyin kasa da lasa da na shiyya shiyya guda 27 ne suka halarci taron. A yayin taron da taken "Hada kai da samun nasara tare, da kafa al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan al'umomin Sin da Afirka", za a tsara shirye-shirye kan wasu muhimman fannonin da bangarorin biyu za su karfafa hadin kai nan da shekaru 3 masu zuwa, da ma nan gaba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China