Mamba a majalisar gudanarwar kasar Sin kuma Ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, da Ministan ciniki Zhong Shan ne suka jagoranci taron tare da ministar harkokin wajen Afrika ta kudu Lindiwe Sisulu da kuma ministan cinikin kasar Rob Davies.
Taron ya samu halartar ministocin harkokin waje ko kuma wakilan kula da harkokin cinikayya da kasashen waje daga kasashen Afrika 53 mambobin dandalin FOCAC da kuma manyan wakilan Tarayyar Afrika. (Fa'iza Mustapha)