in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Sin da Kwadibwa sun yi shawarwari
2018-08-30 13:52:49 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Kwadibwa Alassane Ouattara yau Alhamis a birnin Beijing, inda suka cimma matsayar cewa, za su yi kokarin ciyar da dangantakar kasashensu gaba zuwa wani sabon matsayi, domin samun moriya tare.

Shugaba Xi ya nuna cewa, taron koli na Beijing na dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka, na maida hankali kan kara raya makomar bil'adama ta bai daya tsakanin Sin da Afirka, wanda ke da babbar ma'ana ga bunkasuwar dangantakar abokantaka ta hadin-gwiwa tsakanin Sin da Afirka bisa manyan tsare-tsare, da ingantuwar hadin-gwiwa tsakanin kasashe maso tasowa.

Xi ya jaddada cewa, kasar Sin ta yabawa Kwadibwa saboda matsayinta kan kasancewar kasar Sin daya tak a duk duniya, kuma tana goyon-bayan Kwadibwa ta samu bunkasuwa ta hanyar da ta dace.

A nasa bangaren kuma, Alassane Ouattara ya ce, kasarsa na matukar goyon-bayan shawarar "ziri daya da hanya daya" da shugaba Xi Jinping ya fitar, kuma tana fatan taimakawa kasashe membobin kungiyar ECOWAS don su shiga cikin ayyukan shawarar "ziri daya da hanya daya".(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China