in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru zata kafa cibiyoyin koyon sana'a ga tsoffin mayakan Boko Haram da suka mika waya
2018-08-27 11:11:46 cri
Ministan kula da yankunan kasa na jamhuriyar Kamaru Paul Atanga Nji ya bayyana cewa, kasarsa zata kafa cibiyar koyar da sana'o'in dogaro da kai a yankin arewa mai nisa domin sauya halayyar tsoffin mayakan 'yan ta'adda na Boko Haram.

Ministan ya bayyana hakan ne a wani sansanin dakarun tsaro na gamayyar kasa da kasa a Mora dake yankin arewa mai nisa na jamhuriyar Kamaru, a lokacin da yake ganawa da wasu tsoffin mayakan kungiyar Boko Haram su 100 da suka aje makamansu.

Ya ce horon da za'a basu zai taimaka musu wajen samun sana'o'in da zasu dogara da kansu.

Paul Atanga Nji yace, shugaba Paul Biya na kasar ya samar da wuraren da za'a horas da matasan inda zasu koyi sana'o'i. Wasu daga cikinsu sun nuna sha'awar koyon aikin noma, da aikin kafinta, da aikin gyaran ababen hawa. Don haka kowane mutum daga cikinsu zai koyi sana'ar da zai iya tsayawa da kafarsa.

A cewar ministan, irin kulawar da aka nunawa tsoffin mayakan 'yan ta'addan ya bayyana a fili irin yadda dakarun sojojin Kamaru ke mutunta hakkin dan adam a wajen tukarar abokan gaba da fursunonin yaki.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China