in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yara a Jamhuriyar Demokradiyyar Cogo dake fuskantar barkewar Ebola na bukatar kulawa ta musammam
2018-08-18 16:42:22 cri
Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya ce barkewar cutar Ebola da ake fama da ita a gabashin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, ta shafi yara, ya na mai kira da a ba su kulawa ta musammam.

An ayyana barkewar cutar a arewacin lardin Kivu ne a ranar 1 ga watan nan, kuma UNICEF ya ruwaito cewa, ya zuwa yanzu, yara 2 sun mutu, yayin da wasu 6 wadanda ake zargin sun kamu da cutar ke karbar magani a wasu cibiyo biyu dake yankin.

Asusun UNICEF da abokan huldarsa, sun horar da jami'ai 90 da suka kware kan nazarin tunani da za su taimaka wajen kula da yara a cibiyoyin kula da masu cutar Ebola.

Wadannan kwararru za kuma su taimakawa yaran bayan an sallame su, wadanda ka iya fuskantar tsangwama a cikin al'ummominsu. Sun kuma shirya gangamin wayar da kai domin saukaka komawar yaran.

Baki daya dai, mutane 70 aka tabbatar ko kuma ake zargin sun kamu da Ebola a yankin arewacin Kivu, inda 44 suka mutu. Har ila yau, akwai wasu 24 da ake jiran sakamakon gwajin da aka yi musu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China