A cewar sanarwar, motar tana kan hanyarta ne ta zuwa wata mahakar zinari kafin daga bisani suka afka kan boma baman da aka girke a gefen hanya. Sojoji 5 da farar hula guda ne suka mutu a sanadiyyar harin.
Babu wanda yayi ikirarin daukar alhakin kaddamar da harin.
A farkon wannan shekarar, wasu mahara da ba'a san ko su wane ne ba suka kaddamar da hare hare kan helkwatar rundunar sojojin kasar da kuma ofishin jakadancin kasar Faransa dake Ouagadougou babban birnin kasar , inda yayi sanadiyyar mutuwar sojoji 8.