in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta jajantawa Kasar Indonesia da iftila'in girgizar kasa ta aukawa
2018-08-08 10:48:46 cri
Gwamnatin Nijeriya ta jajantawa al'umma da gwamnatin Indonesia bisa iftila'in girgizar kasa da ta aukawa kasar a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 105.

Ministan harkokin wajen kasar Geoffrey Onyeama, ya bayyana jajen ne a jiya, lokacin da Jakadan Indonesia a Nijeriya Harry Purwanto ya kai masa ziyara a Abuja, babban birnin kasar.

A cewarsa, suna mika jajajensu ga al'umma da Gwamnatin Indonesia a wannan lokaci da suke cikin mawuyancin hali, kuma suna musu fatan samun juriya da hakuri.

Kawo yanzu, girgizar kasar mai karfin maki 7.0 ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 105 da jikkata wasu 236, yayin da hukumomi a kasar suka kwashe masu yawon bude ido 4,600 daga tsibirai 3 dake kusa da Lambok. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China