in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dubban al'ummar Habasha ne suka yi wa Injiniyar da aka kashe mai jagorantar aikin babban madatsar ruwan kasar ban kwana
2018-07-30 10:48:42 cri
Dubban al'ummar Habasha ne suka fita kan titunan birnin Addis Ababa a jiya Lahadi, domin ban kwana da Injiniyan da aka kashe, wanda ke jagorantar aikin ginin babbar madatsar ruwan kasar.

An ratsa da akwatin gawar Simegnew Bekele ta titunan birnin Addis Ababa, inda kuma aka binne shi a babbar mujami'ar Cathedral ta kasar.

An samu gawar Injiniyan cikin motarsa da raunin harbi a ka, a ranar Alhamis da ta gabata.

Gomman masu makoki ciki har da shugaban kasar Mulatu Tshome ne suka yi ban kwana da marigayin.

Bekele, ya kasance babban Injiniyan dake jagorantar babbar madatsar ruwan Habasha mai karfin mega watt 6,450 tun da aka fara aikin a watan Afrilun shekarar 2011 a cikin Kogin Blue Nile.

Idan aka kammala aikin wanda a yanzu ke kan kashi 66 bisa 100 na kammaluwa, zai zama irinsa mafi girma a nahiyar Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China