in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi na ziyarar sada zumunci a Mauritius
2018-07-28 16:24:08 cri

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping, ya isa Kasar Mauritius a jiya Juma'a, a wata ziyarar sada zumunci

Da isarsa, Shugaba Xi ya ga irin kaunar da al'umma da Gwamnatin Mauritius ke wa al'ummar Sinawa.

A cewarsa, Kasar Sin da Mauritius sun dade suna hulda ta abota a tsakaninsu, da kuma kan batutuwan da suka shafi kasa da kasa da yankunansu da kuma wadanda suka shafe su.

Da yake masa maraba, Shugaba Jugnauth na Mauritius, ya ce ya ji dadin karbar bakuncin Shugaban kasar Sin, kuma ya na sa ran ganawa da shi a yau Asabar.

Mauritius ce kasa ta karshe da Shugaba Xi Jinping zai je a ziyararsa ta farko tun bayan da aka sake zabarsa ya shugabanci kasar Sin a karo na 2 a cikin watan Maris. Xi Jinping ya kai ziyara Hadaddiyar Daular Larabawa da Senegal da Rwanda da Afrika ta kudu, ya kuma halarci taron kolin Kungiyar BRICS karo na 10 da ya gudana a birnin Johannesburg. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China