in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran tace Trump ya bukaci ganawa da Rouhani
2018-07-19 12:31:10 cri
Babban jami'in fadar shugaban kasar Iran Mahmoud Vaezi ya sanar a jiya Laraba cewa shugaban kasar Hassan Rouhani ya samu sakonni kimanin 8 daga shugaban kasar Amurka na neman ganawa dashi.

Vaezi yace, shugaba Donald Trump na Amurka ya gabatarwa Rouhani bukatar ne a lokacin da ya kai ziyara New York don halartar babban taron MDD a watan Satumbar 2017, kamar yadda jaridar Tehran Times daily ta wallafa.

Sai dai bai yi cikakken bayani ba, game da ko Rouhani ya amince da goron gayyatar neman ganawar da Trump ya gabatar masa.

A watan Satumbar shekarar 2013, Rouhani da tsohon shugaban kasar Amurka Barack Obama, suka zanta ta wayar tarho a lokacin babban taron MDD karo na 68. Tattaunawar ita ce mafi girma data gudana tsakanin shugabannin kasashen biyu a cikin shekaru sama da 30.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China