in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da rasuwar Sinawa 41 a hadarin kifewar kwale-kwale a Thailand
2018-07-09 09:55:29 cri
Ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Thailand ya tabbatar da cewa, ya zuwa karfe 9 na safiyar jiya Lahadi agogon wurin, Sinawa 41 ne suka rasa rayukansu sakamakon hadarin kifewar kwale-kwale a tsibirin Phuket dake kasar Thailand. Kawo yanzu, hadarin ya yi sanadin mutuwar mutane 42, kana wasu 14 kuma sun bace.

Jiya Lahadi da safe, kungiyoyi biyu dake aikin ceto daga kasar Sin ne suka fara gudanar da ayyukan ceto. Masu aikin ceton suna amfani da na'urorin musamman don gudanar da ayyuka a yankin ruwan tekun da hadarin ya auku.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China