A wani labarin kuma, sojojin sun yi nasarar dakile wani hari da 'yan ta'addan suka yi shirin kaiwa jiya Lahadi a yankin Bama dake jihar ta Borno.
Sai dai Kakakin sojojin kasa na Najeriya Birgediya janar Texas Chukwu ya bayyana cewa, fararen hula guda biyu sun gamu da ajalinsu wasu uku kuma sun jikkata lokacin da sojojin ke kokarin dakile wannan hari.
Chukwu ya ce, mayakan Boko Haram 32 sun mika wuya a wasu cibiyoyin Soja dake jihar Borno, inda ake tantance su kafin a mika su ga hukumomin da suka dace. (Ibrahim)