in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na goyon bayan kara azama wajen yakar ayyukan ta'addanci
2018-06-29 13:13:24 cri
Jiya ne, aka yi wani babban taron manyan jami'an kula da harkokin yaki da ta'addanci na kasashe membobin MDD a hedikwatar Majalisar dake birnin New York.

A jawabin da ya gabatar, wakilin dindindin na kasar Sin a dake MDD, jakada Ma Zhaoxu ya ce kasarsa na goyon-bayan kasa da kasa su kara karfin murkushe ayyukan ta'addanci.

Ma Zhaoxu ya ce, ta'addanci wani babban makiyin bil'adama ne. A don haka ya zama dole kasashen duniya su zama tsintsiya madaurinki daya wajen raya makoma ta bai daya ga daukacin bil'adama. A yayin taron, Ma ya gabatar da wasu muhimman shawarwarin kasar Sin kan yadda za'a yi don kara karfin murkushe ayyukan ta'addanci, ciki har da cimma matsaya daya a fannin yaki da ta'addancin, da daukar matakai daga dukkan fannoni, da karfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashe daban-daban, da aiwatar da yarjeniyoyin da abun ya shafa da sauransu.

Ma ya kuma alkawarta cewa, kasarsa za ta ci gaba da samar da tallafi ga kasashe masu tasowa a fannin yaki da ta'addanci, da hada kai kafada da kafada da sauran kasashen duniya, domin wanzar da zaman lafiya a fadin duniya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China