in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yang Jiechi ya gana da ministar tsaron Afirka ta Kudu
2018-06-29 10:41:11 cri
Jiya Alhamis, a birnin Durban na kasar Afirka ta Kudu, memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana darektan ofishin kwamitin kula da harkokin wajen kasar, Yang Jiechi, ya gana da ministar tsaro na kasar Afirka ta Kudu, Dipuo Letsatsi-Duba, a gabannin halarta taron manyan wakilai kan harkokin tsaro na kasashen BRCIS karo na 8.

Yang Jiechi ya ce, bana shekara ce ta cika shekaru 20 da kulla dangantakar diflomasiyya tsakanin Sin da Afirka ta Kudu. Ana saran Shugaba Xi Jinping zai je Afirka ta Kudu a watan Yuli don halartar taron shugabannin kasashen BRICS karo na 10, sa'annan a watan Satumban bana, shugaba Xi da takwaransa na Afirka ta Kudun, Cyril Ramaphosa za su shugabanci taron koli na Beijing na dandalin tattaunawar Sin da Afirka wato FOCAC. Kasar Sin na fatan karfafa hadin-gwiwa da mu'amala da Afirka ta Kudu, don cimma nasarar shirya wadannan ayyuka biyu, da kokarin habaka huldar kasashen biyu.

A nata bangaren, Duba ta ce, kasarta za ta yi kokarin inganta hadin-gwiwa tsakanin kasashen BRICS da Afirka gami da kasar Sin.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China