in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana goyon bayan matakan gwamnatin Afghanistan na samar da zaman lafiya
2018-06-27 13:43:48 cri
Jakadan kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya ce kasarsa tana fatan gwamnatin Afghanistan za ta cimma yarjejeniyar sasantawa da kungiyoyin 'yan tawaye masu dauke da makamai, ciki har da kungiyar Taliban, daga bisani kuma ta kaddamar da shirin sasantawa.

Manzon na Sin wanda ya bayyana hakan yayin zaman muhawarar kwamitin sulhun MDD game da kasar ta Afghanistan, ya ce kamata ya yi kungiyar Talibin ta shiga a dama ta ita a shirin wanzar da zaman lafiyar da gwamnatin Afghanistan ta bullo da shi, kana ta ba da gudummawar ganin an samar da zaman lafiya a kasar.

Ya ce, sasantawa, ita ce hanya mafi dacewa ta warware batun kasar. Kasar Sin a nata bangare tana goyon bayan shirin da gwmnati da al'ummar kasar suka amince da shi na samar da zaman lafiya da sasantatawa.

Jami'in na Sin ya ce a matsayinta na dadaddiyar kawa dake makwabtaka da Afghanistan, kasar Sin tana fatan ganin an samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da tsaro da ma ci gaba cikin sauri a kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China