Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya tabbatar da cewa, za a kaddamar da taron manyan jami'ai karo na 15 domin tabbatar da "sanarwar aikin sassa daban daban kan batun kudancin teku" a birnin Changsha na lardin Hunan na kasar Sin a ranar 27 ga wata.
Jami'in wanda ta bayyana hakan yayin taron ganawa da manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing, ya kara da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da yin musanyar ra'ayoyi da kasashen mambobin kungiyar ASEAN, game da abubuwan da suke shafar sanarwar, da yadda za a sa kaimi ga hadin gwiwa kan teku, da kuma ka'idar aikin kudancin teku.(Jamila)