Kakakin sojin Ayoub Qassem, ya shedawa manema labarai a wannan rana cewa, jiragen ruwa guda biyu dake dauke da 'yan cin rani ba bisa doka ba daga kasashen Afrika da dama sun lalace, inda suka tsaya a sararin tekun dake yammacin kasar. Sojoji masu gadin gabar tekun ne suka ceto wadannan mutane 301.
Qassem ya ce, an kai 'yan cin ranin wani sansanin sojin ruwa dake birnin Tripoli hedkwatar kasar, inda daga baya za a kai su ofishin yakar shigar 'yan cin rani ba bisa doka ba na kasar. (Amina Xu)